Abubuwan da suka kamata ku sani game da sabon yunƙurin yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza
Abubuwan da suka kamata ku sani game da sabon yunƙurin yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza
Shirin ya tanadi tsagaita wuta na tsawon kwanaki 60, inda za a sako mutane 28 daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da su daga Isra'ila, waɗanda suka haɗa da rayayyu da matattu a mako na farko, sai kuma a saki fursunoni 1,236 na Falasɗinawa da gawawwaki.
30 Mayu 2025

Ana ƙara samun sabon karsashi a cikin awanni 48 da suka gabata game da ƙoƙarin diflomasiyya don kawo karshen yakin Gaza , wanda aka karfafa da wani sabon shirin tsagaita wuta da Amurka ta goyi baya.

Duk da cewa Isra'ila da Hamas suna nuna sha'awa, hanyar tunkarar zaman lafiya tana cike da rashin amincewa ta siyasa, bala'in jin kai, da kuma bukatun asali da ba a magance ba.

Fadar White House ta bayyana a ranar Alhamis cewa Isra'ila ta amince da shirin tsagaita wuta da jakadan Amurka Steve Witkoff ya gabatar, kuma yanzu ana jiran amsa a hukumance daga Hamas.

Shirin ya tanadi tsagaita wuta na tsawon kwanaki 60, inda za a sako mutane 28 daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da su daga Isra'ila, waɗanda suka haɗa da rayayyu da matattu a mako na farko, sai kuma a saki fursunoni 1,236 na Falasɗinawa da gawawwakin Falasdinawa 180.

Sakin zai gudana a matakai biyu—rana ta farko da rana ta bakwai—ba tare da wani taron jama'a ba.

Shirin kuma ya ambaci isar da agajin jinƙai kai tsaye zuwa Gaza, wanda Majalisar Dinkin Duniya da Red Crescent za su kula da shi.

Wata yarjejeniyar tsagaita wuta ta watanni biyu ta rushe a tsakiyar watan Maris bayan Isra'ila ta kaddamar da hare-haren sama a Gaza.

Me ake cewa?

A ranar Alhamis, Karoline Leavitt, mai magana da yawun Fadar White House, ta tabbatar da cewa Isra'ila ta “amince” da shirin, wanda daga bisani aka miƙa wa Hamas ta hannun jakadan yankin Gabas ta Tsakiya na gwamnatin Trump, Steve Witkoff.

Shirin ya samu shiga tsakanin Qatar da Masar.

Wani babban jami'in Hamas ya ce shirin bai cika manyan buƙatun kungiyar ba, kuma za a bayar da amsa ta hukuma nan ba da jimawa ba.

Gwamnatin Isra'ila ba ta fitar da wata sanarwa ba a hukumance. Bisa ga rahoton BBC da tashar talabijin ta Isra'ila Channel 12 sun ruwaito cewa Netanyahu ya sanar da iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su a Gaza cewa Isra'ila ta amince da shirin tsagaita wuta.

Ofishin Netanyahu daga baya ya zargi wani ɗan jarida da ƙoƙarin “shigar da na’urar ɗaukar sauti ba bisa ƙa’ida ba” cikin taron.

Duk da haka, sanarwar ba ta musanta cewa ya amince da shirin Amurka ba, in ji rahoton BBC.

Netanyahu ya taɓa bayyana cewa yakin zai kare ne kawai idan an sako dukkan waɗanda aka yi garkuwa da su, an rusa ko an kwace makaman Hamas, kuma shugabanninta sun bar kasar.

Hamas ta nuna “matsananciyar damuwa,” tana mai cewa yarjejeniyar ba ta cika manyan bukatunsu ba waɗanda suka haɗa da yarjejeniyar tsagaita wuta ta dindindin, janyewar Isra'ila daga Gaza gaba daya, da kuma damar samun agajin jinƙai ba tare da wata cikas ba.

Hamas ta shaida wa Reuters cewa tana nazarin shirin a halin yanzu kuma ana sa ran za ta bayar da amsa ta hukuma zuwa ranar Jumma’a ko Asabar.

Bassem Naim, wani mamba na ofishin siyasa na Hamas, ya bayyana shirin a matsayin ci gaba da “kashe-kashe da yunwa,” yana mai cewa bai magance bukatun asali na al’ummar Falasdinawa ba.

Wani majiyar kusa da kungiyar ya ce sabon shirin “ana daukarsa a matsayin koma baya” daga wanda ya gabata, wanda ya hada da “alkawarin Amurka game da tattaunawar tsagaita wuta na dindindin,” in ji rahoton AFP.

Me ke faruwa a ƙasa?

Duk da cewa tattaunawar tana nuna alamun fata, halin jinƙai a Gaza na ƙara taɓarɓarewa.

Ko da yake agaji ya fara shiga bayan fiye da watanni biyu na takunkumin Isra'ila, rashin abinci ya kai wani mataki mai tsanani.

Yayin da yunwa ke ƙara ƙamari, kusan dukkan mazauna Gaza miliyan 2.3 suna fama da rashin abinci mai gina jiki, daya cikin biyar na Falasdinawa a Gaza na fuskantar yunwa, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

Asusun Jinƙai na Gaza (GHF), wanda Isra'ila da Amurka suka goyi baya, ya fuskanci suka saboda tsarinsa na son-kai da na soja.

A cikin kwanaki biyu da suka gabata, sojojin Isra'ila sun buɗe wuta a kusa da wuraren rabon kayan agaji na GHF a Rafah da Deir al-Balah, inda suka jikkata Falasdinawa sama da 50 kuma suka kashe akalla uku.

Duk da sassaucin da Isra'ila ta yi kwanan nan na takunkumin makonni 11, wanda ya ba da damar shigar da agaji ta Majalisar Dinkin Duniya da GHF, daga cikin manyan motoci 800 da aka amince da su, kusan 200 ne kawai suka isa ga Falasdinawa saboda rashin tsaro da matsalolin dabaru.

A cikin awanni 48 da suka gabata, hare-haren sojojin Isra'ila sun tsananta, kuma tsarin kiwon lafiya na Gaza ya kusan rushewa gaba ɗaya.

A sansanin 'yan gudun hijira na Nuseirat, wani hari a wani tsohon wurin mai da ya zama mafaka ga iyalai da suka rasa matsuguni ya kashe akalla mutane 15, a cewar BBC.

Wani hari a Deir al-Balah ya kashe mutane 13 daga iyalin Abu Samra, ciki har da mata da yara.

A ranar Alhamis, sojojin Isra'ila sun ba da umarnin kwashe mutanen da ke asibitin Al-Awda da ke Tel al-Zaatar a arewacin Gaza—asibiti na karshe da ke aiki a yankin.

Bisa ga rahoton jami’an asibitin, mutum 97 suna ciki a lokacin, ciki har da marasa lafiya 13 da ma’aikatan lafiya 84, kamar yadda The Guardian ta ruwaito.

Asibitin, wanda ya cika da wadanda suka jikkata kuma ya kare da kayan aiki, yanzu ya daina aiki.

Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta ruwaito cewa sama da mutum 54,000 sun mutu tun farkon rikicin, yawancinsu mata da yara.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta yi gargadi cewa tsarin kiwon lafiya na Gaza ya “kai ga karyewa,” inda kashi 94 cikin 100 na asibitoci suka lalace ko aka rusa.

Ma’aikatan lafiya suna yin tiyata ba tare da ba wa mutane maganin sa barci ba, kuma kayan aiki masu muhimmanci sun yi ƙaranci.

A halin yanzu, shirin tsagaita wuta yana cikin hali na rashin tabbas.

Yayin da sama da Falasdinawa 54,000 suka mutu, ita ma Gaza yawanci ta zama kufai, ana kara matsin lamba don samun mafita.

Amma sai dai idan bangarorin biyu sun samu matsaya ta tsakiya, wahalar fararen hular Gaza—da kuma rashin tabbas na siyasa—zai ci gaba.

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us