Hare-hare a jihar Filato da ke arewa maso tsakiyar Najeriya sun yi sanadin mutuwar aƙalla mutane 20 a wannan makon, kamar yadda hukumomin yanki da majiyoyin agaji suka bayyana a ranar Laraba.
Hare-haren uku da aka kai a ƙaramar hukumar Mangu sun biyo bayan jerin hare-hare da ramuwar gayya da aka fara tun lokacin da mutane ke haƙar ma’adanai a yankin da ke da arzikin tin, kamar yadda shugaban ƙaramar hukumar, Emmanuel Bala ya bayyana wa kamfanin dillancin labarai na AFP.
An jima ana samun rikici tsakanin makiyaya da manoma a jihar Filato, kan samun damar amfani da filaye da albarkatun ƙasa.
Hare-hare a yankin galibi suna da alaƙa da ƙabilanci da addini, waɗanda ke haifar da ramuwar gayya tsakanin ɓangarori daban-daban.
Ramuwar Gayya
“A wani lokaci a baya, mutanen yankin suna haƙar ma’adanai, sai aka kai musu hari” da adduna, duk da cewa babu wanda ya mutu a lokacin, in ji Bala ga AFP.
Bayan jerin hare-hare da ramuwar gayya, an samu hare-hare guda uku a ranar Litinin da Talata, wanɗanda suka yi sanadin mutuwar aƙalla mutane 20, in ji Bala.
A daren Talata, mutane takwas sun mutu a ƙauyen Chinchin sakamakon wani hari da ake zargin Fulani ne suka kai, in ji Bala.
Wannan harin ya biyo bayan wani hari da aka kai a wajen garin Langai a ranar Litinin, inda mutane biyar suka mutu.
Makiyaya Fulani a yankin suma sun fuskanci hare-hare da cin zarafi a kwanakin baya, bayan hare-haren da ake zargin wasu daga cikin kabilar su ne suka kai, in ji Bala.
Mummunar gwagwarmaya kan filaye
Haka kuma a ranar Litinin, wasu mahara da ba a san ko su waye ba sun kashe mutane bakwai a yankin Bwe.
Wani jami’in Red Cross ya tabbatar da adadin mutanen da suka mutu a Chinchin kuma ya ce yawan waɗanda suka mutu a cikin sa’o’i 24 zai iya kaiwa 21.
Filayen da manoma da makiyaya ke amfani da su a tsakiyar Najeriya suna fuskantar ƙalubale daga sauyin yanayi da ƙaruwar yawan jama’a, wanɗanda ke haifar da gasa mai tsanani kan taƙaitattun filayen.
Harin ramuwar Gayya
Ƙwace filaye, da rikice-rikicen siyasa da tattalin arziki tsakanin mazauna yankin da waɗanda ake ɗauka a matsayin baƙi, da kuma ƙaruwar masu wa’azin addinai masu tsattsauran ra’ayi, sun ƙara raba kan jama’a a cikin ‘yan shekarun nan.
Idan tashin hankali ya ɓarke, rashin karfin ‘yan sanda na iya haifar da ramuwar gayya, wanda galibi ke faruwa tsakanin al’ummomi daban-daban.
A watan Afrilu kaɗai, hare-hare da aka kai a Filato da jihar Benue da ke maƙwabtaka sun yi sanadin mutuwar fiye da mutane 150.