Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya yi maraba da kalaman da takwaransa na Amurka, Donald Trump ya yi kan kawo ƙarshen rikicin Isra'ila da Iran, yana mai jaddada buƙatar ɗaukar mataki nan take don hana wata babbar masifa da za ta iya mamaye yankin baki ɗaya.
Shugabannin biyu sun tattauna kan rikicin Isra'ila da Iran da batun dangantakar ƙasashen biyu da batutuwan yankin a wata tattaunawar waya, in ji Hukumar Sadarwa ta Turkiyya a shafinta na X a ranar Lahadi.
Erdogan ya sake nanata cewa diflomasiyya ita ce hanya mafi dacewa don warware batun shirin nukiliyar Iran, yana bayyana shirye-shiryen Ankara na yin duk abin da zai yiwu don cimma wannan, ciki har da bayar da tallafi.
Shugaban Turkiyya ya ce hare-haren Isra'ila kan Iran sun haifar da "babbar asarar tattalin arziki da rayukan fararen hula" ga ɓangarorin biyu, yana mai jaddada buƙatar kawo ƙarshen wannan hanya mai haɗari.
Trump, a wani rubutu da ya wallafa a Truth Social a ranar Lahadi, ya ce "Iran da Isra'ila ya kamata su cim ma yarjejeniya, kuma za su cim ma yarjejeniya," yana mai bayyana cewa ana gudanar da kira da taruka da dama don samun zaman lafiya.
‘Mataki na gaggawa’
Rikicin tsakanin Iran da Isra'ila ya fara ne a farkon ranar Juma'a lokacin da Isra'ila ta kai hari kan wuraren soji da nukiliyar Iran, inda ta kashe manyan kwamandoji da masana kimiyya da dama.
Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare, yayin da Iran ta mayar da martani da hare-hare.
Trump da Erdogan sun kuma yi magana ta waya a ranar Asabar.
“Dole ne a ɗauki ‘mataki na gaggawa’ don hana rikicin Iran da Isra'ila mamaye Gabas ta Tsakiya,” in ji Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan a wata tattaunawa da takwaransa na Amurka Donald Trump.