TURKIYYA
2 minti karatu
Shugaban Turkiya Erdogan ya yi Allah wadai da harin Isra'ila kan Iran
A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Juma’a, Erdogan ya ce, “Isra’ila ta ɗauki matakin nutsar da yankinmu — musamman Gaza — cikin jini, hawaye, da rashin kwanciyar hankali zuwa wani mataki mai matuƙar haɗari a safiyar yau.”
Shugaban Turkiya Erdogan ya yi Allah wadai da harin Isra'ila kan Iran
Ya sake jaddada matsayin Turkiyya na adawa da ƙarin rikici a Gabas ta Tsakiya / Anadolu Agency
13 Yuni 2025

Shugaban Ƙasar Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya yi tsokaci mai tsanani kan hare-hare ta sama da Isra'ila ta kai wa Iran, inda ya kira waɗannan hare-haren a matsayin masu babban hatsari da ka iya zama barazana ga zaman lafiyar dama.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Juma’a, Erdogan ya ce, “Isra’ila ta ɗauki matakin nutsar da yankinmu — musamman Gaza — cikin jini, hawaye, da rashin kwanciyar hankali zuwa wani mataki mai matuƙar haɗari a safiyar yau.”

Ya bayyana hare-haren da aka kai wa makwabciyar ƙasar Iran a matsayin “wata fitina a fili da ba ta mutunta dokokin duniya,” yana mai nuna cewa an kai hare-haren ne a wani lokaci mai muhimmanci yayin da tattaunawar nukiliya ke ƙaruwa, kuma matsin lamba na duniya kan ayyukan Isra’ila a Gaza yana ƙaruwa.

“Waɗannan hare-haren sun bayyana irin rashin bin doka da gwamnatin Netanyahu ke yi,” in ji Erdogan, yana gargadin cewa ayyukan Isra’ila na “rashin hankali da tsokana” suna tura yankin da duniya baki ɗaya cikin haɗari.

‘Muna Allah wadai da hare-haren banza da aka kai wa makwabciyar mu Iran’

Yayin da yake kira ga al’ummar duniya su ɗauki mataki, Erdogan ya bayyana cewa: “Al’ummar duniya dole ne su kawo ƙarshen halayen Isra’ila na rashin bin doka da ke barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali na yankin da duniya baki ɗaya. Dole ne a dakatar da hare-haren da Netanyahu da ƙungiyarsa ta kisa ke kaiwa, waɗanda ke ƙona yankin.”

Ya sake jaddada matsayin Turkiyya na adawa da ƙarin rikici a Gabas ta Tsakiya, “Muna sake bayyana cewa ba ma son ganin ƙarin zubar jini, lalacewa, da rikici a Gabas ta Tsakiya.”

Erdogan ya kammala da nuna goyon baya ga Iran, “A matsayinmu na Turkiyya, muna Allah wadai da munanan hare-haren da aka kai wa makwabciyar mu Iran, muna mika ta’aziyyarmu ga mutanen Iran masu aminci, muna roƙon rahamar Allah ga waɗanda suka rasa rayukansu, da samun sauƙi cikin gaggawa ga waɗanda suka jikkata.”

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us