TURKIYYA
1 minti karatu
Girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 6.2 ta afka wa Istanbul, ba a samu rahoton ɓarna ba
Game da girgizar ƙasar da aka yi a Istanbul, ina miƙa fatana na alheri ga ‘yan ƙasarmu, kuma muna sa ido kan yadda abubuwa ke wakana, in ji Shugaba Recep Tayyip Erdogan.
Girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 6.2 ta afka wa Istanbul, ba a samu rahoton ɓarna ba
Hukumar ba da agaji ta gaggawa ta Turkiyya AFAD ta ce an tattara dukkan jami’ai da hukumomi masu ruwa da tsaki domin gane iya ɓarnar da girgizar ƙasar ta yi da kuma tabatar da tsaron jama’a / TRT World and Agencies
23 Afrilu 2025

Girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 6.2 ta afka wa gundumar Silivri da ke birnin Istanbul na ƙasar Turkiyya, in ji hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasar (AFAD).

Girgizar ƙasar ta faru ne da misalin ƙarfe 12.49 na rana na ƙasar (misalin ƙarfe 0949 a agogon GMT) kuma an ji girgizar a faɗin Istanbul ranar Laraba da kuma jihohi masu maƙwabtaka, lamarin da ya sa mazauna birnin suka tsere cikin tsoro.

An kuma samu wata girgizar ƙasar mai ƙarfin maki 4.9 da misalin ƙarfe 1.02  na rana a ƙasar (misalin ƙrfe 10:02 na safe agogon GMT), wanda ya auku a kusa da tekun Buyukcekmece a kogin ​​Marmara.

 

AFAD ta ce an tattara dukkan hukumomi da jami’ai masu ba da agaji kuma an fara gwaje-gwaje domin gano ɓarnar ko kuma tsaron jama’a.

Hukumar ta jaddada cewa jami’a suna sa ido kan lamarin kuma suna jagorantar matakai bisa lamarin. Ba a samu rahoton mutuwa ko rauni ba nan-take ko kuma wata babbar ɓarna.

A wata sanarwa, Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya ce hukumomi suna sa ido kan yadda lamarin ke wakana.

 

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us