NIJERIYA
2 minti karatu
An kashe fiye da mutum 100 a wani harin da aka kai Jihar Benue da ke Nijeriya
Wasu mutane ɗauke da makamai, da ake zargin makiyaya ne, sun afka wa al'ummar Yelewata a Ƙaramar Hukumar Guma a ranar Juma’a da daddare inda suka ci gaba da kai harin har zuwa safiyar Asabar.
An kashe fiye da mutum 100 a wani harin da aka kai Jihar Benue da ke Nijeriya
Ma'aikatan lafiya na kira cikin gaggawa ga mutane su bayar da gudummawar jini don ceton rayukan wadanda suka jikkata / Reuters
15 Yuni 2025

Akalla mutane 102 ne aka kashe a wani hari da aka kai wa wata al'umma a Jihar Benue da ke tsakiyar Nijeriya, a cewar jami'an yankin da kuma shaidu a ranar Asabar.

Wasu mutane ɗauke da makamai, da ake zargin makiyaya ne, sun afka wa al'ummar Yelewata a Ƙaramar Hukumar Guma a ranar Juma’a da daddare inda suka ci gaba da kai harin har zuwa safiyar Asabar.

Wannan harin yana ɗaya daga cikin mafi muni da aka gani a 'yan watannin nan a rikicin da ya dade yana gudana tsakanin manoma da makiyaya a Nijeriya, wanda ya tsananta saboda rikice-rikice kan filaye, samun ruwa, hanyoyin kiwo, da lalacewar amfanin gona.

"Mun rasa mutane aƙalla 102, kuma fiye da 100 suna cikin mawuyacin hali a Asibitin Koyarwa na Jami'ar Jihar Benue (BSUTH) da ke Makurdi," in ji Dennis Denen Gbongbon, Shugaban Kungiyar Manoma Benue Valley, a wata hira ta waya da aka yi da shi.

"Ma'aikatan lafiya na kira cikin gaggawa ga mutane su bayar da gudummawar jini don ceton rayukan wadanda suka jikkata."

‘Babban baƙin ciki’

Wani wanda ya tsira, wanda ya bayyana sunansa da Godspower, ya ce: "Mutanen ɗauke da makamai sun zuba fetur kafin su banka wa gidajenmu wuta, suka kona mutane yayin da suke barci."

Mazauna yankin sun ce harin ya ɗauki fiye da sa'o'i biyu, inda aka lalata gidaje kuma iyalai suka makale a cikin gine-ginen da ke ci da wuta.

Joseph Har, mai ba gwamnan Jihar Benue shawara na musamman kan tsaro da harkokin cikin gida, ya tabbatar da faruwar lamarin kuma ya ce hukumomi har yanzu suna tantance girman harin.

"Mun san da wannan mummunan al'amari da ya faru a safiyar yau, kuma muna binciken kisan fiye da mutane 100. Mun gano gawawwaki 102," in ji Har.

Kakakin 'yan sandan jihar Benue, Udeme Edet, ya ce an tura jami'an tsaro zuwa yankin.

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us