TURKIYYA
1 minti karatu
Erdogan ya yi gargaɗin cewa yaƙin Isra’ila zai iya janyo matsalar gudun hijira da hatsarin nukiliya
Harin Isra’ila ya ƙara barazana sosai ga tsaron yankin, kamar yadda Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya shaida wa shugaban Jamus Friedrich Merz a tattaunawarsu ta wayar tarho
Erdogan ya yi gargaɗin cewa yaƙin Isra’ila zai iya janyo matsalar gudun hijira da hatsarin nukiliya
Hare-haren Isra’ila za su iya lahani ga yankin da kuma Turai dangane da gudun hijira da kuma yoyon nukiliya / Anadolu Agency
20 Yuni 2025

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya ce jerin matsaloli da hare-haren Isra’ila suka haifar za su iya lahani ga yankin Turai game da gudun hijira da kuma yiwuwar yoyon nukiliya.

A tattaunawar da suka yi ta waya da Shugaban Jamus Friedrich Merz, Erdogan ya ce kamata yayi a warware rashin jituwar nukiliya da Iran ta hanyar tattaunawa kuma ya yi gargaɗin cewa hare-haren Isra’ila sun ƙara zama barazana ga tsaron yankin, in ji hukumar sadarwa ta Turkiyya.

"Shugaban ƙasarmu ya kuma yi gargaɗin cewa tashin hankalin da hare-haren Isra’ila suka haddasa za su iya mummunan tasiri a yankin da kuma Turai, musamman game da yiwuwar gudun hijira da kuma abin da ke iya biyo bayan [matsalar] nukiliya," kamar yadda hukumar ta wallafa a shafinta na X.

Shugaba Erdogan ya ce matsalar, wadda ta fara da harin Isra’ila a kan Iran, ya zama barazana ga tsaron yanki.

Shugabannin biyu sun kuma tattauna dangantakar da ke tsakanin ƙasashensu da kuma batutuwa na yanki, in ji hukumar.

 

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us