Wata ƙungiya mai alaƙa da Al Qaeda da ke aiki a yankin Sahel na Afirka ta Yamma ta ɗauki alhakin wani hari da aka kai kan sansanin sojoji a Mali a ranar Lahadi, wanda wasu majiyoyi suka ce harin ya yi sanadin mutuwar sojoji fiye da 30.
Tun farkon watan Mayu, an ruwaito cewa fiye da sojoji 400 sun rasa rayukansu a hannun 'yan bindiga a sansanoni da garuruwa a Mali, Nijar, da Burkina Faso.
Kungiyar JNIM ta bayyana a wata sanarwa a ranar Lahadi cewa ta ƙwace sansanin sojoji a Boulkessi, a tsakiyar Mali, kusa da iyakar Burkina Faso.
Rundunar sojojin Mali ta ce an tilasta mata janyewa.
"Mutane da yawa sun ta gwagwarmaya, wasu har a numfashinsu na ƙarshe, don kare ƙasar Mali," in ji sanarwar, ba tare da bayar da adadin waɗanda suka mutu ba.
Wani mai magana da yawun rundunar bai amsa tambaya kan adadin waɗanda suka mutu ba, amma wasu majiyoyin tsaro biyu sun ce fiye da sojoji 30 ne suka rasa rayukansu.
Wata majiya daga Mondoro, kusa da sansanin, ta ce 'yan bindigar sun "ƙwace sansanin" kuma akwai gawawwaki da yawa.
Sabbin hare-hare
Bidiyoyi da aka yaɗa a yanar gizo sun nuna 'yan bindiga da dama suna mamaye sansanin.
JNIM ta ɗauki alhakin jerin hare-hare a yankin kwanan nan.
A ranar 24 ga Mayu, ta ce ta kai hari a sansanin Dioura, a tsakiyar Mali, inda ta kashe sojoji 40.
A ranar Juma'ar da ta gabata, ta ce ta kwace sansanin Sirakorola a kudu maso yammacin Mali, duk da cewa sojojin sun ce sun dakile harin. Ba su bayar da adadin waɗanda suka mutu ba a wannan lamarin.
A ƙasar Burkina Faso da ke maƙwabtaka, JNIM ta ɗauki alhakin hare-hare kan wuraren da sojoji suke da kuma garin Djibo a tsakiyar Mayu, inda ta ce ta kashe sojoji 200.
A Nijar kuma, fiye da sojoji 100 sun mutu a hare-hare biyu a yankin Tahoua a ranar 24 ga Mayu da yankin Dosso a ranar 26 ga Mayu, in ji majiyoyin tsaro.
Har yanzu Burkina Faso da Nijar ba su wallafa adadin waɗanda suka rasu ba a hukumance.