GABAS TA TSAKIYA
1 minti karatu
Iran na son faɗaɗa dangantakarta da Saudiyya - Ministan Waje na Iran
Ministan harkar wajen Iran ya aika sako zuwa ga takwaransa na Saudiyya, yana nuna sha'awar Tehran ta ƙarfafa dangantaka a dukkan fannoni.
Iran na son faɗaɗa dangantakarta da Saudiyya - Ministan Waje na Iran
Diplomatic representation between Iran and Saudi Arabia resumed in September 2023, for the first time since they severed ties in 2016. / AA
2 Yuli 2025

Iran ta bayyana cewa tana son fadada dangantakarta da Saudiyya a dukkan fannoni.

Wannan sanarwar ta fito ne a cikin wani saƙo da Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, ya aika wa takwaransa na Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan, a ranar Laraba.

A cewar gidan talabijin na gwamnati a Iran, jakadan Iran a Riyadh, Alireza Enayati ne ya mika saƙon ga Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Saudiyya, Waleed bin Abdulkarim Al-Khereiji.

Saƙon ya mayar da hankali kan “bunkasa da ƙarfafa dangantaka a dukkan fannoni,” in ji gidan talabijin ɗin.

An sake farfaɗo da wakilcin diflomasiyya tsakanin Iran da Saudiyya a watan Satumban 2023, bayan shekaru bakwai da katsewar dangantaka tun 2016.

Saudiyya da Iran sun sanar da dawo da dangantakar diflomasiyya a ranar 10 ga Maris na 2023, bayan tattaunawar da China ta jagoranta a birnin Beijing.

Riyadh ta katse dangantaka da Tehran a 2016 bayan hare-haren da aka kai kan ofishin jakadancinta a babban birnin Iran da kuma ofishin jakadancinta a birnin Mashhad na arewa maso gabas.

Hare-haren sun biyo bayan kisan fitaccen malamin Shia, Sheikh Nimr al-Nimr, wanda aka yanke wa hukunci kan “laifukan da suka shafi ta’addanci.”

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us