GABAS TA TSAKIYA
5 minti karatu
Abin da ya kamata a sani game da hare-haren da Isra'ila ta ƙaddamar kan Iran
Isra’ila ta rufe sararin samaniyarta kuma ta ce tana kira ga dubban sojoji don kare iyakokin kasar.
Abin da ya kamata a sani game da hare-haren da Isra'ila ta ƙaddamar kan Iran
Iran ta lashi takobin mayar da martani dangane da harin da Isra'ila ta kai mata / AP
13 Yuni 2025

Isra'ila ta ƙaddamar da wani babban hari kan Iran, wanda ya ƙara fito da rikicin da ƙasashen suke yi a bayan fage na tsawon lokaci zuwa rikici na fili, wanda zai iya rikiɗewa zuwa yaki mai girma a yankin.

Harin da aka kai da safiyar Juma’a ya haddasa fashe-fashe a birnin Tehran, yayin da Isra’ila ta bayyana cewa ta kai hari ne kan cibiyoyin nukiliya da na sojan Iran.

Kafofin watsa labarai na gwamnati a Iran sun ruwaito cewa shugaban Rundunar Juyin Juya Halin Iran da wasu manyan masana kimiyyar nukiliya guda hudu sun mutu.

Harin Isra’ila ya zo ne a lokacin da rikici ya ƙara tsananta kan shirin nukiliyar Iran da ke kara haɓaka cikin sauri, wanda Isra’ila ke kallo a matsayin barazana ga rayuwarta.

Gwamnatin Trump ta sake farfaɗo da ƙoƙarin tattaunawa don taƙaita aikin haɓakar uranium na Iran a madadin sassauta takunkumin tattalin arziki. Amma tattaunawar kai tsaye tsakanin jakadun Amurka da na Iran ta tsaya cik. Wannan hari ya jefa yankin cikin wani sabon yanayi mai cike da rashin tabbas.

Me muka sani zuwa yanzu?

Isra’ila ta kai hari kan wuraren nukiliya, ta kashe shugaban Rundunar Juyin Juya Hali. Shugabannin Isra’ila sun ce an kai harin ne don hana Iran mallakar makamin nukiliya yayin da ƙasar ke ƙara haɓaka uranium ɗinta zuwa matakin da ya kusa zama na makami. Iran ta daɗe tana cewa shirin nata na zaman lafiya ne, kuma hukumomin leƙen asirin Amurka sun yi hasashen cewa Iran ba ta aiki kan ƙera makamin nukiliya.

A wani bidiyo da ya sanar da hare-haren, Firaiminista Benjamin Netanyahu na Isra’ila ya ce hare-haren sun faɗa kan cibiyar inganta uranium ta Natanz da ke Iran, tare da kai hari kan manyan masana kimiyyar nukiliya na kasar.

Ya kuma bayyana cewa Isra’ila ta kai hari kan makaman roka na Iran. Kafofin watsa labarai na gwamnati a Iran sun ruwaito cewa shugaban Rundunar Juyin Juya Hali, Janar Hossein Salami, ya rasu. Mazauna Tehran sun ruwaito jin manyan fashe-fashe. Talabijin ta gwamnatin ƙasar ta nuna hotunan bangon gine-gine da suka rushe, rufin da ke ci da wuta, da tagogi da suka farfashe a cikin gine-gine.

Isra’ila ta rufe sararin samaniyarta

A shirye-shiryen ramuwar gayya, Isra’ila ta rufe sararin samaniyarta kuma ta ce tana kira ga dubban sojoji don kare iyakokin kasar. Netanyahu ya yi ikirarin cewa idan ba a dakatar da Iran ba, “za ta iya ƙera makamin nukiliya cikin kankanin lokaci.” Amma yana yiwuwa Iran ta dauki watanni kafin ta kera makami, idan ta zabi yin hakan.

Makaman Nukiliya

Rikici kan ci gaban nukiliyar Iran da kuma karuwar adadin uranium mai matukar haɓaka ya kara tsananta shekaru bakwai bayan Shugaba Donald Trump ya janye Amurka daga yarjejeniyar nukiliyar Tehran ta 2015 da manyan kasashen duniya.

A karon farko cikin shekaru ashirin, hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya ta yi wa Iran gargaɗi kan rashin bin ƙa’idojin hana yaɗuwar makaman nukiliya da aka tsara don hana ta ƙera makamin nukiliya. A martanin, Iran ta ce za ta bude wata sabuwar cibiyar haɓakar uranium da ba a bayyana ba kuma ta kara samar da uranium mai haɓakar kashi 60 cikin 100, wanda za a iya sarrafa shi cikin sauki zuwa kashi 90 cikin 100 da ake amfani da shi wajen kera makamin nukiliya.

Wuraren Nukiliyar Iran sun daɗe da zama wani wurin rikici. Iran tana da manyan wuraren haɓakar uranium guda biyu, Natanz, a lardin Isfahan na tsakiya, da Fordow, kusa da birnin Qom mai tsarki na Shi’a, kimanin kilomita 90 kudu maso yammacin Tehran. Dukansu an tsara su ne don karewa daga hare-haren sama.

Natanz an gina shi a karkashin kasa a Filin Tsakiyar Iran, kuma an kai masa hare-hare da dama da ake zargin Isra’ila ce ta yi, da kuma cutar kwamfuta ta Stuxnet, wadda ake kyautata zaton Isra’ila da Amurka suka kirkira, wadda ta lalata injinan haɓakar uranium na Iran. Fordow yana cikin tsauni mai zurfi kuma yana da kariya daga makaman sama. Hakanan yana dauke da injinan haɓakar uranium, amma ba babbar cibiya ba ce kamar Natanz.

Trump Ya Gargadi Netanyahu

Duka wuraren sun kasance a tsakiyar kokarin gwamnatin Trump na baya-bayan nan don tattauna sabuwar yarjejeniyar nukiliya da Tehran. Trump ya ce ya gargadi Netanyahu kan kai hari kan wuraren nukiliyar Iran yayin da ake ci gaba da kokarin diflomasiyya.

Ana sa ran jakada na musamman na Amurka Steve Witkoff zai gana da takwarorinsa na Iran a Oman don fara zagaye na shida na tattaunawa a ranar Lahadi. Ba a tabbatar ko tattaunawar za ta ci gaba ba.

Iran Ta Yi Barazanar Ramuwar Gayya

Awanni bayan ƙaddamar da hare-haren, Jagoran Juyin Juya Halin Iran Ayatollah Ali Khamenei ya yi barazanar cewa Isra’ila za ta fuskanci “hukunci mai tsanani.”

Ya bayyana cewa sojoji masu ƙarfi na Jamhuriyar Musulunci ba zai bari (hare-haren) su wuce ba tare da hukunci ba,” in ji jagoran a cikin wata sanarwa da aka wallafa a intanet.

Sauran jami’an Iran sun maimaita gargaɗinsa, suna alƙawarta ɗaukar fansa.

Gidan talabijin na gwamnati ya nuna hotunan ‘yan Iran suna rera wakar “Mutuwa ga Isra’ila!” da “Mutuwa ga Amurka!” Daga Washington, Trump ya ce Amurka ba ta da hannu a harin kuma ya gargadi Iran kan daukar fansa.

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us