AFIRKA
3 minti karatu
'Yan tawayen Rwanda da ke samun goyon bayan DRC sun kashe fararen hula, in ji Human Rights Watch
Mutanen da aka kashe su 21 sun hada da maza shida da mace daya da aka harba a kai a kusa da sansaninn sojoji na Katindo a Goma a ranar 22 ga Fabrairu, a cewar HRW a cikin rahoton da suka fitar.
'Yan tawayen Rwanda da ke samun goyon bayan DRC sun kashe fararen hula, in ji Human Rights Watch
The conflict in eastern DRC is rooted in the spillover of 1994 genocide against in Rwanda and the struggle over DRC's vast mineral resources. / AP
3 Yuni 2025

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Bil'adama ta Human Rights Watch ta bayyana cewa, mayakan M23 da ake zargin suna samun goyon bayan Rwanda sun kashe aƙalla fararen hula 21 a cikin kwanaki biyu a watan Fabrairu a birnin Goma, da ke gabashin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo (DRC).

Rahoton da aka wallafa ranar Talata ya bayyana abubuwan da suka faru a ranakun 22 da 23 ga Fabrairu a wani yanki na Goma, yana nuna irin tashin hankalin da ya faru yayin da rikicin da ya daɗe yana ci-gaba da ruruwa.

“Dole ne a gurfanar da kwamandoji da mayakan da suka bayar da umarnin ko suka aikata waɗannan laifukan a gaban shari’a,” in ji Human Rights Watch a cikin rahoton.

Mayakan M23 sun ƙwace manyan biranen gabashin DRC guda biyu, Goma da Bukavu, tun bayan wani farmaki da suka fara a watan Janairu. Wannan lamari mara misaltuwa ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane tare da tilasta wa daruruwan dubban mutane tserewa daga gidajensu.

Daga cikin fararen hula 21 da aka kashe, akwai maza shida da mace ɗaya da aka harbe su a kai kusa da sansanin sojoji na Katindo a Goma ranar 22 ga Fabrairu, a cewar HRW, mayakan M23 ne suka aikata hakan, bisa ga shaida daga wani ganau.

A wani lamari daban, mayakan M23 sun kashe mutane tare da jefar da gawawwakinsu a wani wajen gine-gine da ke kasa da mita 100 daga sansanin sojoji. Cikin waɗanda aka kashe akwai wani yaro ɗan shekara 15 da aka ɗauka daga gidansa, daga baya aka gano gawarsa a wajen, in ji HRW bisa ga bayanan wani ɗan uwa da makwabcinsa.

HRW ta ce unguwar Kasika a Goma ta kasance a cikin waɗanda aka kai wa hari saboda a baya akwai sansanin sojojin DRC a wajen.

A ranar 23 ga Fabrairu, tashin hankalin ya ci gaba a unguwar lokacin da mayakan M23 suka tattara matasa kusan 20 a wani filin wasanni kusa da wajen. Wani ganau ya shaida wa HRW cewa mayakan sun zargi matasan da kasancewa sojojin gwamnati. Uku daga cikinsu da suka yi ƙoƙarin tserewa an harbe su.

HRW ta ce adadin mutanen da suka mutu a Goma zai iya fin haka yawa, inda ma’aikatan lafiya suka ruwaito cewa an tattara gawawwaki fiye da 50 daga yankin Kasika a cikin kwanaki biyu.

Kungiyoyi daban-daban sun ruwaito wasu manyan laifuka da aka aikata a gabashin DRC tun bayan da M23 ta kwace wasu yankuna.A watan Maris, Amnesty International ta ce mayaƙan sun kai hari asibitoci a Goma don neman sojojin DRC da suka ji rauni, inda suka ɗauki mutane 130 ciki har da ma’aikatan jinya. Wasu daga cikinsu an azabtar da su, yayin da wasu har yanzu ba a san inda suke ba.

UNICEF ta ruwaito ƙaruwar yawan cin zarafin mata da aka yi wa magani a cibiyoyin kiwon lafiya 42 a gabashin DRC a watan Fabrairu, tana bayyana hakan a matsayin mafi muni da aka gani a shekarun baya-bayan nan. Kusan kashi ɗaya bisa uku na waɗanda aka ci zarafinsu yara ne, in ji UNICEF.

Alal misali, wata uwa ta bayyana cewa wasu maza da ke neman abinci ɗauke da makamai sun yi wa ‘ya’yanta mata guda shida fyaɗe, mafi ƙarancin shekarunsu 12.

Rikicin a gabashin DRC ya samo asali ne daga tasirin kisan kiyashin 1994 da aka yi wa ‘yan ƙabilar Tutsi a Rwanda da kuma fafutukar mallakar albarkatun ƙasa masu yawa na DRC.

Rwanda ta musanta zargin Majalisar Ɗinkin Duniya cewa tana goyon bayan M23, tana mai cewa sojojinta suna kare kansu ne daga sojojin DRC da kuma ƙungiyoyin ‘yan tawaye da ke haɗin gwiwa da su.

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us