20 Yuni 2025
Ɗaruruwan ‘yan ta’adda ɗauke da makamai, da yawan su a kan babura, sun kai hari kan wani sansanin sojin Nijar da ke kusa da iyakar Mali, inda suka kashe aƙalla sojoji 34 da jikkata wasu 14.
Maharan - da ma’aikatar tsaro ta kira ‘yan ta’adda - sun yi amfani da motoci takwas da babura 200 wajen kai harin a sansanin da ke Bani-bangou, kamar yadda tashar talabijin din ƙasar ta sanar.
Ba ta bayyana wacce ƙungiyar ta’adda ce ta kai harin ba. Nijar, kamar sauran ƙasashen Sahel na Yammacin Afirka, na fama da ‘yan ta’adda da ke da alaƙa da Alqa’eda da Daesh.
Bayan kai harin, sojoji sun kai farmakai ta sama da ta ƙasa don amintar da yankin, in ji ma’aikatar ba tare da bayar da cikakken bayani ba game da harin.