AFIRKA
2 minti karatu
Sudan ta umarci jami'o'i a birnin Khartoum su koma aiki
Hukumomin ƙasar Sudan sun ba da umarnin gudanar da cikakken nazarin ɓarnar da aka yi a gine-ginen jami'o'i da cibiyoyin bincike da ke babban birnin ƙasar Khartoum.
Sudan ta umarci jami'o'i a birnin Khartoum su koma aiki
The war, which erupted in April 2023, has severely impacted Sudan's higher education sector. / Getty Images
17 Yuni 2025

Firaministan Sudan, Kamil El-Tayib Idris ya umarci Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Binciken Kimiyya da su yi aiki don sake buɗe jami’o’i a babban birnin ƙasar, Khartoum, kamar yadda Sudan News Agency ta ruwaito.

Umarnin ya haɗa da ɗaukar matakai don tantancewa da gyara babbar ɓarnar da aka yi wa gine-ginen jami’o’i da cibiyoyin bincike.

Yaƙin da ya ɓarke a Sudan a watan Afrilu na shekarar 2023 ya yi matuƙar shafar fannin ilimi na ƙasar, inda aka ruwaito cewa an lalata ko kuma an yi wa wasu cibiyoyi a Jihar Khartoum mummunan lahani da ba za a iya gyarawa ba.

Firaminista Kamil El-Tayib Idris ya kuma umarci Cibiyar Kasa ta Manhajoji da Binciken Ilimi da su shigar da darussa a cikin manhajar makarantu, waɗanda za su jaddada muhimmancin ƙarfafa haɗin-kan ƙasa, da kuma gujewa maganganun ƙiyayya.

Sake farfadowar ƙasa

Hukumomi ba su bayyana takamaiman ranar sake buɗe jami’o’in ba, amma sun ce wannan wani muhimmin mataki ne na farfaɗowar ƙasa gabaɗaya.

Rikicin neman mulki tsakanin Rundunar Sojojin Sudan (RSF) da wasu rundunonin sojojin ƙasar ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane, tare da jefa Sudan cikin ɗaya daga cikin mafi munin rikice-rikicen jin-ƙai a duniya.

Fiye da mutane 20,000 sun rasa rayukansu, yayin da aka raba mutane miliyan 15 da muhallansu, kamar yadda Majalisar Ɗinkin Duniya da wasu hukumomin cikin gida suka bayyana.

A watan Fabrairu, sojojin Sudan sun yi saurin sake karɓe babban birnin ƙasar, Khartoum, inda suka tilasta wa RSF ja-da-baya.

Sai dai a makon da ya gabata, RSF ta bayyana cewa ta ƙwace yankin “Triangle” mai muhimmanci, wanda ke haɗa Sudan, Libya, da Misra, bayan wata arangama da sojojin ƙasar.

Sojojin ƙasa sun tabbatar da cewa sun janye daga yankin iyaka “a matsayin wani tsari na kariya don daƙile hare-hare,” kamar yadda Anadolu News Agency ta ruwaito.

Sojojin ƙasar sun zargi dakarun kwamandan sojojin Libya, Khalifa Haftar, da goyon bayan RSF, suna kiran hakan “abin tir” da kuma “sabon take doka ta ƙasa-da-ƙasa.”

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us