AFIRKA
1 minti karatu
An kashe fiye da mutum 40, har da yara a hari kan asibiti a Sudan: WHO
An kai harin a asibitin Al Mujlad da ke yankin West Kordofan ranar Asabar kusa da inda aka ja daga tsakanin sojin Sudan da kuma rundanar RSF, waɗanda suke yaƙi tun watan Afrilun shekarar 2023.
An kashe fiye da mutum 40, har da yara a hari kan asibiti a Sudan: WHO
An kashe yara shida da ma’aikatan jinya biyar a harin / Reuters
24 Yuni 2025

An kashe fiye da mutum 40, ciki har da yara da ma’aikatan jinya a harin da ka kai wani asibiti a Sudan a ƙarshen mako, in ji shugaban hukumar lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya (WHO).

Hari na ranar Asabar kan asibitin Al Mujlad ya faru ne a yankin West Kordofan, kusa da inda aka ja daga tsakanin sojin Sudan da rundunar RSF, waɗanda suke yaƙi tun watan Afrilun shekarar 2023.

Babba daraktan WHO Tedros Adhanom Ghebreyesus ya yi kira da a dena kai hare-hare kan ababen more rayuwa, ba tare da cewa ko wane ne ke da alhaƙin yin hakan ba.

Ofishin WHO a Sudan ya ce an kashe ƙananan yara shida da ma’aikatan jinya biyar a harin, yana mai ba da rahoton cewa an lalace wurin sosai.

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us