AFIRKA
1 minti karatu
An yi jana’izar sojojin Nijar huɗu da aka kashe a harin Diffa
Kamfanin dillancin labaran Nijar ya rawaito a ranar Talata cewa bayan da aka yi musu jana’iza ta addini sai kuma aka yi wa sojojin jana’izar ban-girma ta soji duk a Diffa.
An yi jana’izar sojojin Nijar huɗu da aka kashe a harin Diffa
An yi jana’izar sojojin Nijar huɗu da aka kashe a harin Diffa
18 Maris 2025

Babban hafsan rundunar sojin Jamhuriyar Nijar (CEMA) Birgediya Janar Moussa Salaou Barmou ya jagoranci jana’izar sojojin ƙasar hudu da aka kashe a yayin wani hari da ‘yan ta’adda suka kai sansanin soji da ke Chetima Wango a daren Litinin 17 ga watan Maris na 2025.

Kamfanin dillancin labaran Nijar ya rawaito a ranar Talata cewa bayan da aka yi musu jana’iza ta addini sai kuma aka yi wa sojojin jana’izar ban-girma ta soji duk a Diffa.

Kazalika, Birgediya Janar Barmou ƙarƙashin rakiyar hafsan sojin ƙasa Kanal-Manjo Maman Sani Kiaou da mataimakin hafsan sojin sama Mr. Moctar Diallo da sauran manyan jami’ai sun ziyarci sojojin da suka ji raunuka waɗanda ke kwance a asibiti suna samun kulawa.

A ranar Litinin ne mayaƙan ISWAP suka ƙaddamar da wani mummunan hari a kan sansanin sojin da ke Chetima Wango a yankin Diffa, inda suka kashe sojoji huɗu tare da jikkata wasu da dama. 

Maharan da ake kyautata zaton suna dauke da muggan makamai, sun nufi sansanin sojin ne a wani mataki na ci gaba da yaƙin da suke yi da jami'an tsaro a yankin.

 

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us