SIYASA
2 minti karatu
An rantsar da kwamandan RSF Dagalo a matsayin shugaban gwamnatin adawa a Sudan
A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, gamayyar ƙawancen da RSF ke jagoranta, ta ce Dagalo ya sha rantsuwar kama aiki a Nyala, babban birnin Jihar Darfur ta Kudu da ke yammacin Sudan.
An rantsar da kwamandan RSF Dagalo a matsayin shugaban gwamnatin adawa a Sudan
An rantsar da kwamandan RSF a matsayin shugaban gwamnatin adawa a Sudan / Reuters
8 awanni baya

An rantsar da kwamandan dakarun RSF Mohamed Hamdan Dagalo a matsayin shugaban gwamnatin adawa a Sudan.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, gamayyar ƙawancen da RSF ke jagoranta, ta ce Dagalo ya sha rantsuwar kama aiki a Nyala, babban birnin Jihar Darfur ta Kudu da ke yammacin Sudan.

Ta ce an rantsar da Abdelaziz Adam al-Hilu a matsayin mataimakin Dagalo, tare da mambobin majalisar shugaban ƙasa mai kujeru 13.

A ranar 26 ga watan Yuli ne gamayyar ƙungiyoyin suka sanar da kafa gwamnatin haɗin gwiwa, ƙarƙashin jagorancin Dagalo.

An sanya hannu kan yarjejeniyar siyasa a Kenya

A watan Fabrairu, RSF da wasu ƙungiyoyin ƙawancenta da dama suka rattaba hannu kan wata yarjejeniyar siyasa a Kenya domin kafa gwamnatin adawa a Sudan, matakin da mahukunta a Khartoum suka yi Allah wadai da shi.

A ranar 14 ga watan Agusta, Kwamitin Sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya ya yi watsi da kafa wata gwamnati mai kama da juna a yankunan da ke hannun RSF a matsayin cin zarafi ga 'yancin kai da ƙasa da kuma yankin Sudan baki ɗaya.

Tun a watan Afrilun 2023 sojojin Sudan da dakarun RSF suke ta gwabza yaƙi wanda ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 20,000 tare da raba aƙalla mutum miliyan 14 da muhallansu, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya da hukumomin yankin.

Bincike daga jami'o'in Amurka ya ƙiyasta adaɗin waɗanda suka mutu ya kai kusan 130,000.

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us