NIJERIYA
1 minti karatu
Jirgin ƙasan Kaduna-Abuja na Nijeriya ya yi hatsari bayan sauka daga layinsa
Hukumar kula da layukan dogo ta Nijeriya, NRC ta ce tuni an tura tawagogin agaji da na jami'an lafiya don kai waɗanda suka jikkata asibiti.
Jirgin ƙasan Kaduna-Abuja na Nijeriya ya yi hatsari bayan sauka daga layinsa
Hatsarin Jirgin kasa a Kaduna
21 awanni baya

Jirgin ƙasan da ke zirga-zriga tsakanin Abuja zuwa Kaduna a Nijeriya ya yi hatsari bayan da ya sauka daga layinsa a ranar Talata.

Lamarin ya faru ne a garin Asham, kamar yadda wani mai amfani da shafin Facebook, Imo Onyekwere ya fara wallafa faruwar lamarin kai-tsaye ta bidiyo a shafinsa.

Hatsarin ya faru da misalin ƙarfe 11 na safe, jim kaɗan bayan tashin jirgin daga Abuja zuwa Kaduna.

A cikin bidiyon, ana iya ganin yadda taragun jirgin suka tuntsura, kuma mutane sun taru a wajen suna kallon abin da ya faru da ƙoƙarin aikin ceto, yayin da wasu da suka fi kama da fasinjoji na tsaye cirko-cirko.

Hukumar kula da layukan dogo ta Nijeriya, NRC ta ce tuni an tura tawagogin agaji da na jami'an lafiya don kai waɗanda suka jikkata asibiti.

Sannan ana tsara yadda za a mayar da sauran fasinjojin Abuja.

Kazalika babu bayanai kan mutuwa ko jikkata sakamakon hatsarin.

Titin jirgin ƙasa na Kaduna-Abuja na daga cikin mafiya zirga-zirga a ƙasar, kuma a shekarun baya bayan nan ya sha cin karo da matsaloli, ciki har da na harin da ‘yan bindiga suka taɓa kai masa a watan Maris ɗin 2022.


Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us