Shugaba Bola Tinubu ya amince da a ƙara saka wasu asibitocin gwamnatin tarayya a tsarinsa na rage kuɗin wankin ƙoda daga ₦50,000 zuwa ₦12,000 wanda ya fara sanarwa a watan Maris ɗin wannan shekarar.
Mai bai wa Shugaban Ƙasar Shawara na Musamman kan Manufa da Watsa Labarai, Daniel Bwala ne ya bayyana hakan a shafinsa na X ranar Litinin.
Ya bayyana cewa “da wannan daukin, kuɗin kowane aiki na wankin ƙoda ya ragu daga N50,000 zuwa N12,000 kacal, lamarin da zai kawo sauƙi ga dubban ‘yan ƙasa da ke fama da cututtukan da suka shafi ƙoda.”
Bwala ya ce tuni an riga an fara aiwatar da tallafin a muhimman asibitocin gwamnatin tarayya 10 a shiyoyin ƙasar shida.
Asibitocin sun haɗa da Cibiyar Lafiya ta Gwamnatin Tarayya da ke Ebute-Metta, a Legas; da Cibiyar Lafiya ta Gwamnatin Tarayya da ke Jabi a Abuja; da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ibadan; da kuma Cibiyar Lafiya ta Gwamnatin Tarayya da ke Owerri.
Kazalika asibitocin sun haɗa da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri da Cibiyar Lafiya ta Gwamnatin Tarayya da ke Abeokuta da Asibitin koyarwa na Jami’ar gwamnatin jihar Legas da Cibiyar Lafiya ta Gwamnatin Tarayya da ke Azare da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Benin da kuma Asibitin koyarwa na Jami’ar Kalaba.
Ya ƙara da cewa za a ƙara shigar da wasu asibitocin koyarwa da cibiyoyin lafiya na tarayya cikin shirin kafin ƙarshen shekarar nan domin faɗaɗa gurbin wankin ƙoda a faɗin ƙasar.
Bwala ya kuma tuna da yadda Tinubu ya ba da damar yi wa mata tiyatar haihuwa kyauta a asibitocin gwamnatin tarayya, a matsayin wani babban mataki na inganta lafiyar uwa da kuma rage mutuwar mata wajen haihuwa.