NIJERIYA
4 minti karatu
Hukumar DSS ta buƙaci shafin X ya cire saƙon da Sowore ya wallafa yana ƙaryata Shugaba Tinubu
Hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta yi iƙirarin cewa magoya bayan Shugaba Tinubu waɗanda saƙon da Sowore ya wallafa ya ɓata wa rai sun fara zanga-zanga a kan titunan Nijeriya.
Hukumar DSS ta buƙaci shafin X ya cire saƙon da Sowore ya wallafa yana ƙaryata Shugaba Tinubu
Mai fafatuka Omoyele Sowore ya ce ba zai goge saƙon da ya wallafa ba / Reuters
6 awanni baya

Hukumar tsaro ta farin kaya ta Nijeriya (DSS) ta rubuta wasiƙa ga kamfanin X Corp, mai shafin sada zumunta na X (wanda ake ce wa Twitter a da), tana mai neman kamfanin ya goge wani saƙo da mai fafatuka Omoyele Sowore ya wallafa inda ya ƙaryata Shugaba Bola Tinubu .

A wata wasiƙar da DSS ta wallafa shafinta na X ranar Asabar, hukumar ta zargi Mista Sowore da yin amfani da saƙonsa na X  wajen cin fuskar shugaban ƙasa Tinubu da yi masa rashin mutunci da ba’a.

A saƙon da ya wallafa a shafinsa na X ranar 25 ga watan Agusta, Mista Sowore ya soki ziyarar da shugaban Nijeriya ya kai Brazil da kuma kalaman da shugaban ya yi yayin ziyarar.

“Mai laifi @officialABAT (Bola Tinubu) ya je Brazil inda ya ce babu cin hanci da rashawa a Nijeriya a gwamnatinsa. Ji wani ƙarfin hali na ƙarya ba tare da kunya ba!”— in ji Omoyele Sowore (@YeleSowore) ranar 26 ga watan Agustan shekarar 2025.

Sai dai a wasiƙar da DSS ta aike wa kamfanin X ta ce waɗannan kalaman sun ɓata wa magoya bayan Shugaba Tinubu rai lamarin da ya sa suka yi zanga-zangar rashin amincewa da kalaman na Sowore a kan titunan ƙasar.

Saboda haka, hukumar ta bai wa shafin X wa’adin sa’o’i 24 domin ya cire kalaman Sowore  ko kuma ta ɗauki matakai masu tsauri a kan shafin.

Kalaman Tinubu a Brazil

A lokacin da ya kai ziyara ƙasar Brazil dai, Shugaba Tinubu ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatinsa ta yi a Nijeriya sun kawo ƙarshen cin hanci a ƙasar.

“Sauyen-sauyen da na ƙaddamar tun da na karɓi ragamar mulki a Nijeriya suna tasiri sosai. Zan iya bugun ƙirji kan haka. Daga farko sun ba da wahala. Amma a yau sakamakonsu yana haɓaka,” in ji Shugaba Tinubu.

 “Yana daɗa bayyana ga mutane. Mun ƙara yawan kuɗi cikin tattalin arzikinmu. Yanzu babu cin hanci da rashawa. Gwamnan babban bankin [Nijeriya] ya zo nan. Ba sai ka san shi ba kafin ka samu takardun kudin ƙasashen waje da kake buƙata,” in ji shi.

“An kawar da ‘yan bunburutu daga kasuwar musayar kuɗaɗenmu. Ƙofa a buɗe take ga cinikayya shiga cikin sauƙi, fita cikin sauƙi,” a cewarsa.

Martanin Sowore

Shi kuwa mai fafatuka, Omoyele Sowore, wanda hukumar DSS take ƙorafi game da saƙon da ya wallafa ya mayar da martani da saƙon DSS.

“Da safiyar yau, X (wadda ake ce wa Twitter a da) ta tuntuɓe ni a hukumance game da wasiƙar barazana da suka samu daga hukumar DSS mara bin doka game da saƙon da na wallafa kan Tinubu. Ba zan goge saƙon ba,” in ji Sowore a saƙonsa na X.

Abin jira a gani shi ne abin da zai faru bayan wa’adin sa’o’i 24 da hukumar DSS ta bai wa X.

Gwamnatin Nijeriya ta taɓa haramta amfani da shafin X

Wannan dai ba shi ne karon farko da aka fara samun sa-in-sa tsakanin gwamnatin Nijeriya da kafar sada zumuntar X ba.

Ko tsakanin shekarar 2021 zuwa shekarar 2022 ma sai da ƙasar ta haramta amfani da shafin na X na watanni bakwai bayan shafin ya goge wani saƙo da shugaban ƙasar Nijeriya na lokacin, marigayi Muhammadu Buhari, ya wallafa a shafinsa na X.

A saƙon nasa da X ya goge Buhari ya ce waɗanda suke neman kafa ƙasar Biafra ba su san irin abin da aka yi ba a lokacin yaƙin basasar Nijeriya kuma gwamnati za ta bi da su ta hanyar da suka fi ganewa.

Bayan goge wannan saƙon ne gwamnatin Nijeriya ta hana amfani da shafin na X a ƙasar, har sai lokacin da shafin ya cika wasu ƙa’idojin da gwamnatin ta gindaya masa.

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us