Isra’ila tana tattaunawa da Sudan Ta Kudu game da yiwuwar tsugunar da Falasɗinawa daga Gaza a ƙasar ta Afirka wacce yaƙi ya ɗaiɗaita, a wani ɓangare na ƙoƙarin Isra’ila wajen tilasta wa ficewar mutane da dama daga birnin da aka yi wa ƙawanya wanda yaƙin watanni 22 ya lalata.
Mutum shida da ke sane da lamarin sun tabbatar da tattaunawar ga kamfanin dillancin labaran Associated Press (AP).
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya ce yana son ya cim ma burin Shugaban Amurka Donald Trump na sauya wa mutanen Gaza wuri ta abin da Netanyahu ya kira “ƙaura ta son kai.” Isra’ila ta gabatar da shawarwari na sake tsugunarwar ga sauran ƙasashen Afirka.
Falasɗinawa da ƙungiyoyin kare ‘yancin dan’adam da kuma da yawa daga cikin ƙasashen duniya sun yi watsi da shawarwarin a matsayin wani shiri na kora da ƙarfin tuwo da ya saɓa wa dokar ƙasa da ƙasa.
Kazalika wannan wata hanya ce da Trump, wanda ya fara kawo maganar sake tsugunar da Falasɗinawan a watan Fabrairu amma da alama ya sauya ra’ayinsa, zai iya bi.
Ma’aikatar Harkokin Wajen Isra’ila ta ƙi ta yi tsokaci game da batun, kuma Ministan Harkokin Wajen Sudan Ta Kudu bai amsa tambayoyi game da tattaunawar ba.
Wani mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ya ce ba ta tsokaci game da tattaunawar sirri ta harkokin diflomasiyyar ƙasashe.