GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Iran ta yi Allah wadai da hare-haren Amurka, ta ce sun saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa
Ministan Harkokin Wajen Iran, Seyed Abbas Araghchi, ya fitar da wata kakkausar sanarwa a ranar Lahadi, inda ya bayyana harin a matsayin “abin kunya” mai “mummunan sakamako na dindindin.”
Iran ta yi Allah wadai da hare-haren Amurka, ta ce sun saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa
Araghchi ya jaddada haƙƙin Iran na mayar da martani bisa Kundin Majalisar Dinkin Duniya, / AP
22 Yuni 2025

Iran ta yi Allah wadai da wani hari da Amurka ta kai kan wuraren nukiliyarta, tana mai kiran hakan babban take haƙƙin dokokin ƙasa da ƙasa.

Ministan Harkokin Wajen Iran, Seyed Abbas Araghchi, ya fitar da wata kakkausar sanarwa a ranar Lahadi, inda ya bayyana harin a matsayin “abin kunya” mai “mummunan sakamako na dindindin.”

Ya zargi Amurka, wacce ke cikin mambobin dindindin na Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, da saɓa wa Kundin Majalisar Ɗinkin Duniya da kuma Yarjejeniyar Hana Yaduwar Makaman Nukiliya (NPT).

“Dukkan mambobin Majalisar Ɗinkin Duniya ya kamata su damu da wannan hali mai matuƙar haɗari, rashin doka da kuma laifin da aka aikata,” in ji Araghchi a cikin sanarwarsa.

Harin, wanda aka kai da sanyin safiyar Lahadi, ya faɗa kan wuraren da Tehran ke cewa ana amfani da su ne don ayyukan nukiliya na zaman lafiya.

Araghchi ya jaddada haƙƙin Iran na mayar da martani bisa Kundin Majalisar Dinkin Duniya, wanda ya ba da damar kare kai daga wani hari na makami.

“Iran tana da dukkan zaɓin da za ta yi amfani da su wajen kare ikon mulkinta, muradunta, da mutanenta,” in ji ministan harkokin wajen.

Tashin hankali tsakanin Washington da Tehran ya kara tsananta bayan harin, wanda ya jawo damuwa daga ƙasashen duniya kan yiwuwar rashin zaman lafiya a yankin.

Shigar Amurka yaƙi

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa sojojin Amurka sun samu nasarar kai hare-hare kan wuraren nukiliya guda uku na Iran, wanda ya haifar da damuwa kan yiwuwar rikici mai fadi a yankin.

Trump ya ce an jefa bama-bamai masu “tsananin nauyi” a kan babban wurin nukiliya na Iran da ke Fordow, sannan an kai wasu hare-hare a wuraren Natanz da Esfahan.

Ya kuma bayyana cewa dukkan jiragen yakin Amurka sun bar sararin samaniyar Iran.

Trump ya kuma yi wa Iran ɗin ƙarin barazana idan ta ce za ta rama harin da aka kai mata.

Yi somin-taɓin a TRT Global. Bari mu ji ra'ayoyinku!
Contact us